10 Yuni 2026 - 21:09
Source: ABNA24
Maariv: Trump Da Netanyahu Sun Gane Ba Zai Yiwu Su Galaba Kan Iran Ba

Jaridar Isra'ila "Maariv" a cikin wani rahoto tana mai ikrari kan tsayin daka da ƙarfin juriyar Iran da Hizbullah ta Lebanon, ta rubuta: Sanya Iraniyawa da Hizbullah su yi biyayya abu ne mai wuya da wahala, kuma wannan yanayin na iya jefa Isra'ila zuwa yaƙi maras ƙarewa. Wannan jaridar a baya ma ta ba da rahoton cewa Trump da Netanyahu sun gane cewa ba zai yiwu su yi nasara kan Iran ba, kuma dole ne su amince da cewa Iran za ta ci gaba da kasancewa babbar ƙasa mai ƙarfin nukiliya a duniya.

Kamfanin Dillancin Labaran ƙasa da ƙasa na Ahlul-Baiti (AS) – ABNA - ya habarta cewa: Jaridar Isra'ila "Maariv" a cikin wani rahoto game da abubuwan da suka faru a shekara da ta wuce, ta yi nuni da cewa tsayin dakar Iraniyawa da Hizbullah ta Lebanon ya tabbatar wa Isra'ila cewa tana fuskantar abokan gaba da ba a zata ba.

A daidai lokacin da ake fitar da wannan rahoto, "Robert O'Brien" tsohon mai ba da shawara kan tsaron ƙasar Amurka shi ma a cikin hira da jaridar Maariv ya ce: Ina ganin muna gab da cimma yarjejeniya da Iran. Da aka tambaye shi ko sakamakon tattaunawar zai iya kai wa ga yarjejeniya irin ta JCPOA? Ya ce: A'a, ina ganin yarjejeniya za ta fi kyau. Ina fata yarjejeniyar da za a kulla za ta iya haifar da daidaita dangantaka da bunƙasar tattalin arziki a yankin kuma ta kawo ƙarshen yaƙi.

Jaridar Maariv a ci gaba da rahotonta na nazari ta bayyana cewa: durkufar da Iraniyawa da Hizbullah abu ne mai wuya da wahala; domin suna da ƙarfin juriya sosai.

Wannan kafar yaɗa labarai ta Isra'ila ta jaddada cewa: Wannan yanayin na iya jefa Isra'ila zuwa yaƙin maras ƙarewa.

Ikrarin Cewa Ba Za A Iya Cin Galaba Kan Iran Ba

Tun da farko ma, jaridar Maariv a cikin wani rahoto game da rashin yiwuwar cin nasara kan Iran ga makiya ta rubuta cewa: Trump da Netanyahu sun gane cewa ba zai yiwu a ci nasara kan Iran ba, kuma dole ne su amince da cewa wannan ƙasa za ta ci gaba da kasancewa babbar ƙasa mai ƙarfin nukiliya.

Wannan jaridar ta kara da cewa: Trump da Netanyahu sun kuma gane cewa Hizbullah za ta ci gaba da wanzuwa, kuma Washington na neman hanyoyin tuntuba da ita. Wannan yana faruwa ne a daidai lokacin da Netanyahu a yanzu kafin zaɓen Knesset (majalisar dokokin gwamnatin yahudawa) ke neman nasara a kan zirin Gaza da mazaunanta da ke zaune a tantuna.

Duk da kusan shekaru uku da da gwamnatin yahudawa fara tayar da zaune-tsaye a yankin, sojojin wannan gwamnati sun makale acikin wannan danbarwar yakin kuma ba su iya cimma burin da aka zayyana na yaƙin ba.

Gwamnatin yahudawa har yanzu tana cikin yaƙi a zirin Gaza da Lebanon, kuma tayar da zaune-tsaye na wannan gwamnati tare da hadin gwiwar Amurka a kan Iran shi ma ya fuskanci martani mai ƙarfi, wanda Tel Aviv da Washington sun gaza cimma burinsu na wannan tayar da zaune-tsaye.

..................

Your Comment

You are replying to: .
captcha